Najeriya: Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Wani Shugaban PDP

Jam’iyyar PDP reshen jihar Legas, ta yi kira ga jami’an tsaro da hukumomin gwamnati da su sa kokari cikin gaggawa don ganin an sako shugaban jam’iyyar da aka sace, Philip Aivoji.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na jihar Legas, Alhaji Hakeem Amode, ne ya yi wannan kira a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, yana mai cewa: “An sace Aivoji ne a ranar Alhamis, 25 ga watan Janairu da misalin karfe 6:00 na yamma a kan hanyar Legas zuwa Ibadan yayin da yake dawowa daga taron masu ruwa da tsaki a jihar Oyo wanda Gwamna Seyi Makinde da Gwamna Ademola Adeleke na Osun suka kira.

“Abin takaici ne yadda garkuwa da mutane ya zama ruwan dare a kasarmu, kuma gazawar gwamnati na magance wannan matsala abin damuwa ne matuka.”

Sace Aivoji ya nuna matukar bukatar daukar kwararan matakai daga gwamnati da masu ruwa da tsaki don kawar da wannan matsalar.”

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...