Mutane Dubu Talatin Zasu Sami Aiki A Kamfanin Dangwate

Kamfanin wanda a yanzu ya share fili mai fadin hekta dubu sittin da takwas zai lakume kudi naira biliyan dari biyu da saba’in kamar yadda gwamnan jahar, Umaru Tanko Almakura ya shaidawa Muryar Amurka.

Sarkin manoman jahar Nasarawa, Alhaji Aliyu Usman yace dalibai da suka kamala karatu basu da ayyukan yi, zasu sami guraben aiki a kamfanin.

Basaraken gargajiya na yankin Awe, Alhaji Abubakar Umar na biyu yace jama’a da dama sun yi na’am da shirin don fiye da matasa dubu daya yanzu suna aiki a gonar, wanda an dauke su aiki kenan.

Ana sa nan da shekaru biyu zuwa uku kamfanin zai fara aiki tukuru.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...