MDD ta bayyana damuwa kan hare-haren Borno da Kaduna

Majalisar Dinkin Duniya(MDD) ta bayyana matukar damuwar ta kan rahotannin dake nuna yadda ake sake samun kashe-kashe daga hare-haren da yan kungiyar Boko Haram suke kai wa a jihar Borno.

A wata sanarwa da jami’in tsare-tsare na Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya ya fitar, Edward Kallon ya ce hare-haren idan ba a kawo karshen su ba za su kawo koma baya kan nasarar da aka samu wajen kare rayukan mutane a yankin arewa maso gabas.

Saboda haka ya shawarci gwamnatin tarayya da kuma jami’an tsaro dake yankin da su kara kokarin da suke na kare fararen hula.

Har ila yau wakilin na Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya ya bayyana damuwarsa kan rikicin kabilanci da ya faru a garin Kasuwar Magani dake kudancin Kaduna da ya haifar da asarar rayukan mutane da dama.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...