Man U ba ta son sayar da Pogba, Lukaku zai daina buga wa Beligium

[ad_1]

Paul Pogba

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Pogba ya koma United ne a shekarar 2016 a kan fam miliyan 89

Manchester United ta ce ba za ta sayar da dan wasan tsakiyarta dan Faransa, Paul Pogba, wanda yake son komawa Barcelona, in ji jaridar (Sun).

Ita kuwajaridarMirror ta ce Arsenal tana da kwarin gwiwar ci gaba da rike dan wasa tsakiyar Wales, Aaron Ramsey, mai shekara 27, duk da cewa Barcelonada Lazio suna son dan wasan.

KocinTottenham Mauricio Pochettino ya shaida wa (Sky Sports) cewa yana ganin wasu ‘yan wasan za su bar kulob din kafin a rufe kasuwar musayar ‘yan wasa duk da cewa Spurs ba ta sayi ko dan wasa daya ba a wannan lokacin bazarar.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Moussa Sissoko (a hagu)

Amma kuma (Talksport) ta ruwaito cewa dan wasan tsakiyar Tottenham,dan Faransa, Moussa Sissoko, mai shekara 29, ya shaida wa magoya bayan kulob din cewa shi zai tsaya a kungiyar.

Pochettino ya kuma ce yana shirin kasancewa da Tottenham na tsawon lokaci bayan ya samu damar koma wa Real Madrid, ko Chelsea a kakar da ta gabata, kamar yadda jaridar (Mirror)ta ruwaito.

Chelsea ta tattauna da dan wasan gaban kungiyarLyon,Nabil Fekir, mai shekara 25, a lokacin bazara, amma a lokacin bazara ta ki sayen dan kasar, Faransan, a cewar (Goal).

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Yaya Toure

Ita kuma jaridar (Sun) ta ambato kocin West Ham, Manuel Pellegrini, yana cewa kungiyarsa ba za ta sayi dan wasan tsakiyar Ivory Coast, Yaya Toure, mai shekara 35, wanda ya kasance ba shi da kulob, tun bayan da ya bar Manchester City.

Dan wasan gaban Manchester United dan kasar Belgium, Romelu Lukaku, mai shekara 25, ya ce yana son ya daina buga wa kasarsa kwallon bayan kammala gasar cin kofin kasashen nahiyar Turai ta Euro, wadda za a yi a shekarar 2020, in ji (Business Insider).

Real Madrid ba ta ji dadin cewa Inter Milan ta tuntubi dan wasanta na tsakiya dan kasar Croatia, mai shekara 32, Luka Modric, ba tare da fara tuntubar kulob dinsa ba, a cewar (Mundo Deportivo).

[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...