Majalisar dokokin jihar kano ta kafa wani kwamiti mai wakilai 7 da zai bincika sahihancin fefan bidiyon dake nuna gwamna, Abdullahi Umar Ganduje yana karbar kudi.
Jaridar Daily Nigerian da ake wallafawa a Intanet ce ta saki fefan bidiyon gwamnan wanda ake zargin yana karbar cin hanci daga yan kwangila.
An kafa kwamitin bayan da wakilin mazabar Warawa a majalisar,Labaran Abdul Madari ya gabatar da kudirin dake buƙatar kulawar gaggawa kuma ya samu goyon bayan, Dr Baffa Babba Danagundi.
Madari ya ce majalisar na da ikon bincike kan duk wani batu da zai shafi zaman lafiya a jihar.
Da yake magana ya yin zaman shugaban marasa rinjaye a majalisar,Baffa Babba Danagundi ya shawarci gwamnatin jihar da ta janye batun gurfanar da Jaridar gaban kotu kan fefan bidiyon.
A cewarsa kundin tsarin mulki ya bawa majalisar ikon binkicen lamari irin wannan.
Kwamitin zai samu shugabancin,Baffa Babba Danagundi.
Kwamitin zai kammala aikinsa cikin wata daya.