‘Legas na cikin biranen da suka fi wuyar sha’ani’

[ad_1]

Hakkin mallakar hoto
AFP

Image caption

Legas ta zo ta 138 cikin birane 140 da aka yi kuri’ar jin ra’ayin jama’a

Binciken shekara-shekara na Mujallar The Economist da ke Burtaniya, ya ce birane 7 cikin 10 na duniya da ba su da dadin zama a nahiyar Afirka su ke.

Binciken da ya wallafa jerin kasashe 140 inda aka aiwatar da bincike a kai, ya yi nazari akan daidaiton siyasa da walwala da miyagun ayyuka da ilimi da wadatuwar kiwon lafiya.

Birnin lagos da ke Najeriya, shi ne na 138-inda mataki 2 ya raba shi da babban birnin Syria wato Damascus da yaki ya daidaita kuma yake mataki na 140 a rukunin kasashen da mujallar ya wallafa.

Birnin Harare na Zimbabwe shi ne ke mataki na 135, yayin da birnin Tripoli a Libya ke mataki na 134, sai Douala a Kamaru da ke mataki na 133.

Sauran sun hada da Algiers na Algeriya da ke mataki na 132, Dakar na Senegal na mataki na 131.

Sai dai birnnin Johannesburg na Afirka ta Kudu da ke mataki na 86 a duniya, ya kasance birnin da yi fi kowanne birni dadin rayuwa a Afirka.

Rahotan da mujallar ke wallafa kowacce shekara ya ce birane a yankunan gabas ta tsakiya da Afirka da Asiya su ne 10 karshe cikin 140 da ke fuskantar karancin kwanciyar hankali, hade da rigingimu da ta’addanci da kuma yaki.

Birnin Melbourne na Australia shi ya fi kowanne dadin rayuwa a duniya a cewar The Economist, yayin da Vienne a Austria ke mataki na Biyu sai Vancouver na Canada da ke na 3.

Kamar yadda rahotan ya nuna kasashen Australiya da Canada kowanne na da birane 3 da rayuwa ke da dadin zama a cikin birane 10 da ke kan gaba a duniya.

Kuma wadanan kasashe biyu ke kan gaba wajen samun farin ciki a duniya kamar yadda rahotan Majalisar dinkin duniya ya bayyana a baya.

Babu birnin Amurka ko guda da ke cikin rukunin 10 farko, sakamakon matsalolin da suka shafi rashin kwanciyar hankali da ke da alaka da mutuwar bakaken fata a hannu jami’an tsaro.

Suma biranen masu alfarma da arziki irin su London da Paris da Tokyo ba sa cikin jerin farko na biranen da ake rayuwa mai dadi a yanzu, saboda karuwar matsalolin tsaro da cunkoson mutane da matsalolin sufuri da ke tasiri ga walwalar al’ummarsu.

[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...