Kwankwaso ya kaddamar da takarararsa a zaben 2019

[ad_1]

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso

Image caption

Kwankwaso ya taba fafatawa da Buhari a zaben fitar da gwani a jam’iyyar APC a shekarar 2014.

Tsohon Gwamnan jihar Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya kaddamar da takarar neman shugabancin Najeriya a babban zaben shekarar 2019.

Dan siyasar ya kaddamar da aniyyar hakan ne a wani filin taro da ke unguwar Jabi a Abuja ranar Laraba.

Sai dai gabanin hakan, a ranar Talata wani jigo a kwamitin yakin neman zaben Sanata Kwanwaso, Kwamred Aminu Abdussalam, ya yi ikirarin cewa hukumomi sun hana tsohon gwamnan jihar Kano din taron siyasa a wurare biyu a Abuja.

Dubban magoya bayan dan siyasar ne suka taru a dandalin da ya bayyana aniyyarsa ta neman tsayawa takarar.

Kwankwaso na cikin mutane da dama da ke son PDP ta tatsayar da su takara domin fafatawa da Buhari a 2019.

Ba wannan ne karon farko dan tsohon gwamnan yake neman shugabancin kasar ba.

Ya fara neman takarar ne a zaben 2015, sai dai ya sha kaye a hannun Shugaba Muhammadu Buhari bayan zaben fidda gwani na jam’iyyar APC.

A cikin watan Yuli ne Sanata Kwankwaso da shugaban Majalisar Dattawan kasar Bukola Saraki da wadansu gwamnoni da ‘yan majalisa da dama suka bar APC zuwa PDP.

Na’urarku na da matsalar sauraren sauti

Rabiu Musa Kwankwaso

[ad_2]

More News

Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

Mutanen Sokoto na ta murnar kashe ƙasurgumin ɗanbindigar nan Halilu Buzu

Mazauna yankin Sokoto da kewaye na murnar kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Halilu Buzu, da sojojin Najeriya suka yi a farmakin da...