[ad_1]
Bayan hana shi yin amfani da filin Eagle Square wajen kaddamar da takararsa ta shugaban kasa, tsohon gwamnan jihar Kano,kuma mai neman takara a karkashin jam’iyar PDP, Rabi’u Musa Kwankwaso ya ci alwashin kaddamar da takarar shugaban kasarsa a yau.
Kwankwaso na neman jam’iyar PDP ta bashi tikitin takarar shugaban kasa a zaɓen fidda gwani na jam’iyar PDP.
Ƙungiyar yakin neman zaben Kwankwaso ta bayar da sanarwar karɓar wata wasika mai dauke da kwanan watan, 27 ga watan Agusta mai dauke da sahannun, Usman Mukhtar Raji na kamfanin Integrated Facility Management Services Ltd, kamfanin dake kula filin na Eagle Square kasa da sa’o’i 24 na kaddamar da takarar shugaban kasar tasa.
Ƙungiyar yakin neman zaben ta ce hakan ba zai hana su kaddamar da takarar ba.
Mai taimakawa gwamnan kan harkokin yada labarai, Hajiya Binta Spikin ta ce duk da hana su kaddamar da takarar da Æ´ansanda suka yi babu gudu babu ja da baya wajen kaddamar da takarar a yau.
[ad_2]