Kasar Jamus Na Taimakawa Wajen Samar Da Zaman Lafiya a Jihar Filato

[ad_1]

A wani taron ‘karawa juna sani wanda ya hada da shugabannin addinai mata da matasa da makiyaya da kuma manoma daga ‘kananan hukumomi biyar da ake yawan samun tashin hankali da ma ‘yan jarida, domin tattaunawa kan musabbabin tashin rikici da ake samu a yankunan da kuma dabarun magancesu.

Mr Akin Omoware, jami’i ne dake aiki a hukumar inganta rayuwar al’umma ta kasar Jamus dake jihar Filato, ya shaidawa Muryar Amurka cewar manufar taron ita ce su ‘kara kwarin gwiwa wa hukumar sasantawa ta jihar Filato ta hanyar horas da masu ruwa da tsaki dabarun fahintar alamun dake haddasa rikici da hanyoyin magancesu ba tare da an samu tashin hankali ba.

Mr Akin, ya ce ba wanda ke amfana da tashin hankali, ko da ma mutum yana ganin kamar akwai ribar da yake samu a yanzu a rikicin dake aukuwa, tabbas watarana zai yi da na sani, saboda duk abin da mutum ya samu ta hanyar rikici, to kuwa ta hanyar rikicin zai rasa shi, don haka dole mu tabbatar mun sanya tubalin da zai taimaka wajen sasantawa da fahintar juna.

Daraktan labarai na gidan rediyo da talabijin mallakar jihar Pilato, Yakubu Tadi ya ce ‘yan Jarida nada gagarumin gudunmowa a harkar tsaro.

Domin karin bayani saurari rahotan Zainab Babaji.

[ad_2]

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da Æ´an ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an Æ´an sanda da kuma sojoji suna É—aukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar Æ´an sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe É—an Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa HaÉ—in Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...