Karyewar babbar gada ta zub da mutane a ruwa

[ad_1]

Wani bangaren rusasshiyar gadar ya fada ne cikin wani tafki.

Hakkin mallakar hoto
EPA

Image caption

Wani bangaren rusasshiyar gadar ya fada ne cikin wani tafki.

Wata babbar gada ta karye a kusa da birnin Genoana na Italiya, abinda ya janyo motoci da dama suka fada cikin ruwa.

Ministan sufurin kasar, Danilo Toninelli, ya ce alamu na nuna cewa hadarin ya yi muni.

Kamfanin dillacin labarai na Adnkronos ya ambato wani jami’in lafiya yana cewa mutane da dama sun mutu.

Hukummomi sun shaida wa AFP cewa mafi yawan wajen da ya karye ya fada ne kan layin dogo na jirgin kasa, inda suka kara da cewa motoci manya da kanana sun fado daga karyayyiyar gadar.

An gina gadar ne a shekarun 1960, kuma akwai dimbin jama’a a garin da da lamarin ya faru.

Gadar dai ta fadi ne lokacin da ake ruwan sama kamar da bakin kwarya.

[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...