Kana da labarin matar da mijinta ya sake ta saboda son Buhari?

Wani magidanci mai suna Abdullahi Yadau ya saki matrsa saboda rashin jituwa dangane da bambancin ra’ayin siyasa a jihar Filato da ke Najeriya.

Abdullahi ya shaida wa BBC cewa ya yi wa matarsa saki biyu ne bayan da ta sha alawashin cewa “ita Shugaba Muhammadu Buhari za ta zaba a zaben 2019.”

Ya ce har sai da maganar ta kai gaban iyayenta, inda daga nan ne sai ya yanke hukuncin sakinta wanda kuma har ya balla mata hakori, a cewarsa.

BBC ta yi kokarin jin ta bakin mai dakinsa Hafsat, sai dai hakan ya ci tura.

Amma mun yi magana da yayanta mai suna Ibrahim Suleiman, wanda ya bayyana bacin ransa game da abin da ya faru.

Da alama zaben 2019 zai fi wadanda suka gabace shi ta fuskar rabuwar kawunan al’umma da ke mara wa mabambantan ‘yan takara baya.

Wasu masu sharhi kan al’amura a kasar suna ganin hakan bai rasa nasaba da yadda duka manyan ‘yan takarar biyu sun fito ne daga yanki guda – wato arewacin kasar.

More News

NDLEA ta kama wani mai safarar hodar ibilis a filin jirgin sama na Kano

Jami'an hukumar NDLEA dake yaƙi da hana sha da kuma fataucin miyagun kwayoyi sun kama wani mutum mai suna, Okafor  Ifeanyi Anthony mai shekaru...

Magoya bayan jam’iyar PDP sun gudanar da zanga-zanga a jihar Edo

Magoya bayan jam'iyar PDP a jihar Edo sun gudanar da zanga-zanga ranar Lahadi a Benin babban birnin jihar kan yadda ake cigaba da tattara...

Magoya bayan jam’iyar PDP sun gudanar da zanga-zanga a jihar Edo

Magoya bayan jam'iyar PDP a jihar Edo sun gudanar da zanga-zanga ranar Lahadi a Benin babban birnin jihar kan yadda ake cigaba da tattara...

Magoya bayan jam’iyar PDP sun gudanar da zanga-zanga a jihar Edo

Magoya bayan jam'iyar PDP a jihar Edo sun gudanar da zanga-zanga ranar Lahadi a Benin babban birnin jihar kan yadda ake cigaba da tattara...