Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.

Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

Soneye ya ce za a dauki ma’aikata ne na mukamai daban-daban a sassa daban-daban na kamfanin makamashi.

Ya umurci masu bukata da su ziyarci shafin ma’aikata na NNPC don cike fom din neman aikin

“NNPC Ltd na farin cikin sanar da cewa a halin yanzu muna daukar ma’aikata da yawa a sassa daban-daban.  Muna neman mutane masu hazaka da sadaukarwa don shiga kamfaninmu.  Ziyarci shafinmu na sana’o’i don neman umarnin cike aikace-aikacen,” in ji Soneye. 

A cikin wani sabon bayanin da ya sake, Soeye ya bayyana cewa saboda yawan zirga-zirgar da ba a taba gani ba a shafin yanar gizon NNPC Ltd daga masu neman guraben aiki, a halin yanzu shafin yana fuskantar tafiyar hawainiya.

“Masana na’urorinmu suna aiki tukuru don gyara matsalar.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...