‘Kada ka yarda ka cire tallafin wutar lantarki’—Ƙungiyar ƙwadago ta faɗa wa Tinubu

Kungiyoyin kwadago da masana’antu da masana tattalin arziki da kudi da shari’a sun gargadi gwamnatin tarayya da kada ta cire tallafin wutar lantarki kamar yadda asusun lamuni na duniya IMF ya shawarta.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke fama da matsalar tsadar rayuwa sakamakon cire tallafin man fetur, bisa shawarar IMF da bankin duniya.

Sai dai, asusun, a rahotonsa na baya-bayan nan, ya shawarci gwamnati don ta kawar da tallafin man fetur da wutar lantarki gaba daya a matsayin wani mataki na magance kalubalen tattalin arzikin da ake fuskanta.

A cikin rahotonta mai taken ‘IMF Executive Board Concludes Post Financing Assessment with Nigeria,’ IMF ta nanata muhimmancin kawar da tallafin don karkatar da albarkatun zuwa shirye-shiryen jin dadin jama’a.

A halin da ake ciki na tsadar rayuwa, IMF ta ba da shawarar tura wa jama’a tallafi don ba da taimako na wucin gadi ga ɓangarorin al’ummar Najeriya masu rauni.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...