Jihar Neja Ta Yi Rajistar Mutane 289 Da Suka Kamu Da Cutar Amai Da Gudawa, 17 Sun Mutu


Wata annobar cutar amai da gudawa a Jihar Neja ta yi sanadin mutuwar mutane 17 tare da kama mutane 289 a kananan hukumomi 11 na jihar, a cewar Kwamishinan Lafiya na Matakin Biyu da na Uku na Jihar Neja, Bello Tukur.

Yanzu haka, mutane 9 suna kwance a asibiti.

Tukur ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga Majalisar Dokokin Jihar Neja dangane da karuwar yawan masu kamuwa da cutar amai da gudawa a Najeriya.

Ya bayyana dabarun da gwamnatin jihar ke amfani da su wajen dakile yaduwar cutar, ciki har da kafa kwamitin musamman domin tsara ayyuka a fannonin kiwon lafiya na matakin farko, na biyu, da na uku.

A cewarsa, jihar tana amfani da fasahar zamani da tsare-tsare masu inganci wajen karfafa shirin ko-ta-kwana kan annobar.

Shugaban Kwamitin Majalisar Dokokin Jihar Neja na Lafiya a matakin Farko da na Biyu, Umar Nasiru, wanda shi ma magatakarda ne, ya gargadi al’umma da su guji duk wani abu da zai iya sa a kamu da cutar, kamar yin bahaya a fili da rashin tsafta.

More News

An ƙona sakatariyar ƙananan hukumomi 2 a jihar Rivers

Wasu da ake kyautata zaton ɓatagari ne sun ƙona wani sashe na sakatariyar ƙananan hukumomin Eleme da Ikwerre dake jihar Rivers. Ƙona ginin na zuwa...

Ƴanbindiga sun hallaka wani shugaban APC a Kebbi

Wasu ‘yan bindiga sun harbe Bako Bala, shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Suru a jihar Kebbi, a yayin wani yunkurin yin garkuwa da...

Kotu ta hana VIO kamawa, tsare motoci ko cin tarar direbobi a kan hanya

Justis Evelyn Maha ta Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta bayar da umarni da ya hana Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa, wanda aka...

Sojojin Najeriya sun hallaka masu haramtacciyar harƙar man fetur

Dakarun runduna ta 6 ta sojojin Najeriya sun kashe wasu mutane biyu da ake zargin barayin man fetur ne, tare da cafke wasu 18...