Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, ta sanar da kama wani da ake zargin manomin ganyen wiwi ne a jihar Sokoto.
Kwamandan hukumar ta NDLEA a jihar, Adamu Iro, ya shaida wa manema labarai a Sokoto a ranar Asabar cewa, “Wannan shi ne karo na farko da irin wannan lamari ya faru a tarihin jihar.”
Mista Iro ya ce an kama wanda ake zargin Anas Sani ne a kauyen Sayinna da ke karamar hukumar Tambuwal, bayan da aka samu labari.
Ya ce wanda ake zargin ya shuka wata irin tabar wiwi na kasar waje a gonarsa ta masara, wadda jami’an NDLEA suka gano.
A cewarsa, za a gurfanar da wanda ake zargin bayan binciken kimiyya na ganyen da aka tumbuke.