Illar Cutar Daji Idan Ba a Dauki Matakin Gaggawa Ba

Zainab Bagudu wacce ke zantawa da manema labarai a Abuja, ta ce ranar Asabar din karshen watan nan za a gudanar da tattakin da gaiyatar mutane musamman ma’aikata da ba sa motsa jiki su fito don takawa da ‘kafa tsawon kilomita 10.

Gidauniyar dai da kan tallafawa masu fama da cutar daji musamman mata da kan samu matsalar a maman su da mahaifa, na samun labarun masu jinyar a birane da karkara, inda ta kan tura a kai mu su dauki.

Zainab Bagudu ta ce maganin ya na da tsadar gaske, don haka ya dace mata su rika duba maman su duk wata don fahimtar lafiya kalau su ke ko da wata alamar larura.

Ita ma hukumar lafiya matakin farko ta taraiya ta bukaci mutane su rika lura da alamun cuta da wuri kamar shan inna da a ke neman gamawa da ita.

Dakta Saidu Adamu, shine jami’in daukin gaggawa na yaki da shan inna, ya ce da zarar an samu labari a kan tura jami’ai don tabbatarwa da daukar matakin da ya dace.

A Najeriya ba mamaki ka ga ginin asibiti amma ba lalle ne akwai wadatattun likitoci da magunguna ba da hakan kan sanya masu hannu da shuni tafiya asibitocin kudi, wasu talakawa kuwa su rika tunkarar magungunan gargajiya don saukin samu.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...