[ad_1]
Gwamnatin Kamaru ta ce ta kama wasu sojoji shida bayan bincike kan wani bidiyon da aka watsa makwannin da suka gabata, da ya nuna yadda wasu sojoji suka ci zarafin fararen hula.
Wata kafar yada labarai ta Kamaru ce ta ruwaito wannan labarin a shafinta na Internet.
Hakan na nuna cewa gwamnatin ta sauya matsayar da ta dauka tun da farko na musanta cewa an kama sojojin.
Ana zargin sojojin shida da hada baki wajen kisan gilla ga mata da kananan yara a yankin Arewa Mai Nisa.
A cikin wani hoton bidiyo da aka ringa watsa wa a kafofin sada zumunta, an gano wasu mutane sanye da kayan sojoji sun harbe mata biyu daya da goyo a bayanta, da kuma wata yarinya.
An jiyo suna zargin matan da dangataka da kungiyar Boko Haram.
Hukumomin Kamaru sun tura sojoji yankin Arewa Mai Nisa da ke makwabtaka da Najeriya, domin yaki da kungiyar Boko Haram.
Kungiyoyin kare hakkin bil adama sun zargi sojojin kamaru da laifukan yaki, a yunkurin murkushe Boko Haram.
[ad_2]