Hukumar Zaben Najeriya Ta Ki Karbar Sunayen ‘Yan Takarar Zamfara

Daidai lokacin da a ke muhawara kan karbar sunayen ‘yan takarar zaben 2019 na APC daga jihar Zamfara, shugaban hukumar zaben Farfesa Mahmud Yakubu ya ce hukumar ba za ta ce komai ba tun da wadanda lamarin ya shafa sun kai kara kotu, amma sam hukumar ba ta karbi sunayen ba.

Farfesa Yakubu na magana ne kan rade-radin cewa jam’iyyar APC ta mika sunayen ‘yan takarar ta daga kan na gwamna zuwa ‘yan majalisar Dattawa da Wakilai, da tun farko hukumar ta ce ba za ta amshi sunayen don saba ka’idar lokacin gudanar da zaben.

Jigo a siyasar APC ta Zamfara Ikra Aliyu Bilbis, ya ce sun kalubalanci matsayin hukumar zaben a kotu don su na da yakinin an gudanar da zaben, da sa ran samun hukunci a ranar Talatar nan.

A tarihi idan hukumar zabe ta dauki mataki kan lamari irin wannan, kotu ce kan zama raba gardama kuma ko ma ta yaya shari’ar ta kaya, ba mamaki wanda bai gamsu ba ya tafi kotun daukaka kara.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...