Gwamnatin tarayya ta bayyana wani shiri na amfani da filaye da ba a amfani da su a manyan makarantu domin noma a wani mataki na bunkasa samar da abinci a fadin ƙasar nan.
Ministan noma da samar da abinci Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a cocin Seventh-day Adventist, yayin taron Eastern Nigeria Union Conference Centenary Public Lecture and Food mai taken ‘’ kawo karshen karancin abinci a Najeriya, yadda za a yi amfani da wanda ba a amfani da shi’ a Fatakwal ranar Juma’a.
Kyari, wanda ya samu wakilcin mataimakin daraktan kula da abinci na ma’aikatar, Nuhu Kilishi, ya ce tuni aka mika wa cibiyoyin wasiku, domin neman yardarsu.
Ya bayyana cewa wasu daga cikin manyan makarantun sun fara nuna yardarsu, yana mai cewa matakin zai zama tabbataccen mataki na farfado da noma a makarantu.
Kyari ya ce, “Muna son farfado da noma a makarantu da cibiyoyi. Mun rubuta wa jami’o’i da makarantu da su bar mu mu yi amfani da kadada na gonakinsu da ba a yi amfani da su ba.