Gwamnatin Tarayya ta musanta rahotannin cewa tana shirin rusa gidaje 1,500 a yankin Xhidu da ke kusa da Lugbe Phase II a Abuja.
Shugaban sashen yada labarai na hukumar kula da gidaje ta tarayya, FHA Kenneth Chigelu ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa.
A makon da ya gabata ne dai aka yi ta yada cewa mazauna unguwar sun yi zargin cewa hukumar ta FHA ta shirya ruguza gidajensu domin wani estet da wani ɗan kasuwa mai zaman kansa zai gina.
A cewar mazauna yankin, matakin na FHA “ya keta haƙƙinsu na tsarin mulki a fili, yana watsi da jin daɗinsu a matsayinsu na ‘yan ƙasa, kuma yana zubar da mutuncin Najeriya a duniya.”
A halin da ake ciki, FHA ta ce ba ita ce ke da alhakin rusa ginin ba.
“Hukumar tana son gyara kuskuren tunanin da wasu manu neman filaye ke yi, wadanda a kullum suke yaudarar wasu ‘yan Najeriya da ba su ji ba ba su gani ba, ta hanyar karbar kudade daga hannunsu tare da sayar da filayen gwamnati.”