Gwamnatin Najeriya za ta biya alawus ɗin N-Power na wata tara

Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na fara biyan bashin watanni tara ga masu cin gajiyar shirin N-Power da ke shirin farawa daga watan Nuwamba.

Ta bayyana hakan ne a ranar Litinin ta bakin Manajan shirye-shiryen N-Power na kasa, Akindele Egbuwalo, wanda ya bayyana hakan a wata ganawa da wasu masu cin gajiyar N-Power a ofishinsa da ke Abuja.

Egbuwalo a wata sanarwa da ma’aikatar kula da jin kai da yaki da fatara ta tarayya ta fitar, ya bayyana cewa babbar manufar dakatar da shirin na wucin gadi shi ne a magance duk wani abu da ya shafi masu cin gajiyar shirin kai tsaye.

A cikin sanarwar ya bayyana cewa, sakamakon dakatar da shirin na wucin gadi da aka yi na yin gyaran fuska da kuma binciken kwakwaf, an kwato kudade daga hannun wasu a ciki.

More News

Jihar Neja Ta Yi Rajistar Mutane 289 Da Suka Kamu Da Cutar Amai Da Gudawa, 17 Sun Mutu

Wata annobar cutar amai da gudawa a Jihar Neja ta yi sanadin mutuwar mutane 17 tare da kama mutane 289 a kananan hukumomi 11...

An ƙona sakatariyar ƙananan hukumomi 2 a jihar Rivers

Wasu da ake kyautata zaton ɓatagari ne sun ƙona wani sashe na sakatariyar ƙananan hukumomin Eleme da Ikwerre dake jihar Rivers. Ƙona ginin na zuwa...

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴanbindiga sun hallaka wani shugaban APC a Kebbi

Wasu ‘yan bindiga sun harbe Bako Bala, shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Suru a jihar Kebbi, a yayin wani yunkurin yin garkuwa da...