Gwamnatin Borno ta yi alƙawarin kammala wasu gidajen ƴan gudun hijira

Gwamna Babagana Zulum na Borno ya tabbatar wa mutanen Logumani da Gajibo da suka rasa matsugunansu cewa nan ba da jimawa ba za a sake mayar da su zuwa yankunansu.

In ba a manta ba, ‘yan Boko Haram sun lalata muhallan al’ummomin biyu a ƙananan hukumomin Ngala da Dikwa, tare da raba ɗaiɗaita yankin tun shekarar 2014.

Sai dai gwamnan ya yi musu albishir, inda ya ce nan ba da jimawa ba za su koma gidajensu bayan kammala ayyukan gina gidaje 1,000 da ake yi.

Ya yi wannan jawabi ne a lokacin da yake duba yadda aikin ke gudana a ranar Juma’a.

Ya ce yana da yakinin cewa za a kammala aikin kuma za a sake mayar da mutane nan da watanni biyu.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...