Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.

Kwamishinan Watsa Labarai, Yarima Okey Kanu, ya bayyana wannan bayani ranar Talata yayin da yake zantawa da manema labarai kan sakamakon taron majalisar zartarwa ta jiha da aka gudanar a ranar Litinin karkashin jagorancin Gwamna Alex Otti.

“Gwamnatin jiha na da cikakken aniyar biyan albashin mafi karanci, kuma saboda haka, a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, za a fara biyan wannan albashi,” inji Kanu.

Kwamishinan Kwadago da Samar da Ayyuka, Sunny Onwuma, ya sake tabbatar da kudurin gwamnatin jihar na biyan albashin mafi karanci na kasa na naira 70,000.

Haka kuma, Kanu ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta amince da sabon aikin gina hanyoyi guda tara a fadin mazabun sanatoci uku na jihar.

More News

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...

Sojojin Najeriya Sun Musanta Jita-jitar Mutuwar Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja

Daga Sabiu AbdullahiRundunar Sojojin Najeriya ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja,...