Gobara ta yi ƙurmus da sansanin yan gudun hijira a Borno

Rahotannin da suke fitowa daga jihar Borno a Arewa maso Gabashin Najeriya na nuna cewa gobara tlalata dukiyoyi da wasu kayayyaki masu daraja a wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke Muna a karamar hukumar Jere a jihar.

An ce gobarar ta tashi ne da sanyin safiyar Laraba.

Wajen da gobarar ta yi ɓarna ke nan

Jami’an Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA), sun kai ziyarar tantance wuraren da lamarin ya faru.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a tantance musabbabin tashin gobarar ba.

Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan wata gobara ta ƙone shaguna da dukiyoyi na miliyoyin naira a babbar kasuwar Gamboru da ke Maiduguri babban birnin jihar Borno.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...