Fitaccen Malamin Addini Dokta Idris Dutsen Tanshi Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

Fitaccen malamin addinin Islama daga Jihar Bauchi, Dokta Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi, ya riga mu gidan gaskiya.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa marigayin ya rasu ne a gidansa da ke Bauchi, inda ake sa ran gudanar da jana’izarsa a safiyar yau Juma’a.

Dokta Idris ya dade yana fama da rashin lafiya, lamarin da ya sa gabanin watan Ramadana ya tafi kasashen Masar da Saudiyya domin neman magani.

A fitowarsa ta karshe da aka gani a bainar jama’a, ya gabatar da huduba a ranar Idin Karamar Sallah da ta gabata, inda ya jaddada muhimmancin hadin kai a tsakanin Musulmi.

Marigayin ya kasance malami mai fada a ji wanda ya yi tasiri a harkokin addini, kuma ya bar tarihi mai kyau a fagen wa’azi da karantarwa.

Allah ya jikansa da rahama, ya gafarta masa kura-kuransa, amin.

More from this stream

Recomended