Hukumar Yaki Da Yiwa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati EFFC ta wallafa wasu hotunan gidaje da take zargin tsohon gwamnan jihar Ekiti Ayodele Fayose ya saya da kudaden haram
Wilson Uwujaren, mai magana da yawun hukumar shi ne ya saki hotunan gidaje ranar Laraba, ya ce an gano gidajen lokacin da hukumar take bincike kan zargin aikata cin hanci da rashawa da a kewa tsohon gwamnan.
Uwujaren ya yi zargin cewa Fayose ya sayi gidajen ne da kudin da tsohon mai bawa shugaban kasa shawara akan harkar tsaro Kanal Sambo Dasuki ya bashi.
“A binciken da muke na zargin aikata cin hanci da rashawa kan tsohon gwamna Fayose musamman kan kudi biliyan ₦1.3 da ya karba daga ofishin mai bawa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro.Hukumar ta bankado wasu hujjoji dake nuna cewa ya karkatar da kudade wajen sayen wasu gidaje a unguwanni masu daraja dake birnin tarayya Abuja,”Wilson ya ce.
A ranar Talata ne dai Fayose ya kai kansa ofishin hukumar dake Abuja dai-dai lokacin da ake rantsar Kayode Fayemi a matsayin sabon gwamnan jihar.