Dakarun Najeriya Sun Dukufa Wajen Gano Gawar Janar Idris Alkali

Dakarun Najeriya, karkashin jagorancin Garizon kwamanda, runduna ta uku dake birnin Jos, Birgediya Janar Ibrahim Muhammad, ya ce binciken da suka fara gudanarwa na nuni da cewar an gano motar Janar Idris Alkali a yankin Dura Du, a karamar hukumar Jos ta Kudu, don haka suka fara yasar wani tafki da suke zaton an jefa motar Janar din.

Janar Muhammad, ya ce sun shafe mako guda kenan suna neman gawar Janar Idris Alkali, da motarsa Toyota Corolla, baka. Ya kara da cewamuna so mu san ko yana raye, wannan bincike da mukeyi na ceto, mun samu bayanai ne cewa an tura wadansu motoci a cikin rafin”.

Yace tun kwana uku kenan muke kokarin ganin ko zamu gano wani abu a cikin rafin amma ganin yadda rafin ya kasance tsohon wurin hakar ma’adinai ne ya kasance da wahala, duk da shike mun yi amfani da babbar motar dake daga abu mai nauyi amma har yanzu bamu gano shi ba. Janar Ibrahim Muhammad ya ce a yanzu haka sun yanke shawarar zasu janye ruwa daga rafin don gano abinda ke karkashin sa.

Janar Muhammad, ya hori al’ummar dake zaune a yankin da su basu hadin kai wajen bankado bata gari a jahar Pilato, ya kuma basu tabbacin jami’an tsaro ba zasu ci mutuncin kowa a yankin ba.

A halin da ake ciki kuma, yayinda sojojin ke yashe tafkin, mata saye da bakaken tufafi sun gudanar da zanga-zanga, wanda a cewarsu ruwan rafin suke amfani dashi yau da kullum. Jagorar matan, Mary Yakubu, ta ce in an yashe ruwan rafin ‘ya’yan su da mazajensu zasu mutu saboda haka basa son kowa ya taba ruwan.

A yanzu haka dai sojojin sun tsaurara matakan tsaro a yankin suna kuma gudanar da aikin yasar tafkin don gano gawar Janar Idris Alkali ko akasin haka.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...