Da ɗumi-ɗumi: Ododo na APC ya lashe zaɓen gwamna a Kogi

An bayyana dan takarar gwamnan jam’iyyar All Progressives Congress, Usman Ododo, a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Kogi da aka kammala ranar 11 ga watan Nuwamba.

Ododo ya samu kuri’u 446,237, inda ya doke abokin hamayyarsa Murtala Ajaka na jam’iyyar Social Democratic Party, wanda ya samu kuri’u 259,052, yayin da Dino Melaye na jam’iyyar PDP ya samu kuri’u 46,362.

Hakan dai na zuwa ne duk da cewa INEC ta sanar da cewa za a sake gudanar da sabon zabe a wasu rumfunan zabe a karamar hukumar Ogori/Magongo da ke jihar a ranar 18 ga Nuwamba, 2023.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...