Ya bayyana hakan ne a cikin wani jawabi a wajen bikin cika shekara 40 da kasar ta kawo manyan sauye- sauya a fannin tattalin arziki.
Ya kuma bayyana cewa kasarsa ba za ta amince wasu kasashe su juya ta ba.
Tsarin tsohon shugaban kasar Deng Xiaoping na son kawo “gyara” ya fara ne shekara 40 da suka wuce.
Tsarin ya fitar da miliyoyin mutane daga talauci, amma a kwanakin baya Chana tana fama da bashi da kuma raguwar habbakar tattalin arziki.