[ad_1]
Shugaban kasa, Muhammad Buhari zai fara hutu na kwanakin aiki 10 daga ranar 3 ga watan Agusta na shekarar 2018.
Shugaban ya aikewa da shugaban majalisar dattawa Abubakar Bukola Saraki da kuma kakakin majalisar wakilai, Yakubu Dogara takardar tafiyarsa hutun kamar yadda sashe na145(1) na kundin tsarin mulkin Najeriya na shekarar 1999 ya tanada.
Yayin da shugaban kasar yake hutun, mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo zai rike mukamin mukaddashin shugaban kasa.
Buhari zai gudanar da hutun nasa a can birnin Landon na kasar Birtaniya.
[ad_2]