Bene Ya Rufta Da Mutane A Abuja

[ad_1]








A yammacin yau Juma’a ne wani bene mai hawa biyar ya rufta a yankin Jabi da ke babban birnin tarayya Abuja.

Rahotanni sun bayyana cewa a lokacin da benen ya rufa, ana kan aiki a cikin sa.

Kimanin mutane hudu aka garzaya da su asibiti yayin da jami’an hukumar bayarda agajin gaggawa ke ci gaba da aikin ceto wadanda abun ya ritsa da su.

Jami’an na yunkurin kwashe baraguzan ginin domin ceto mutanen da ginin ya danne.

Wasu rahotannin sun nuna cewa cikin wadanda lamarin ya rutsa da su har da mata.

Izuwa lokacin da aka wallafa wannan labari, ba a san adadin mutanen da wannan abu ya ritsa da su ba.

Haka zalika ba a san musabbin zubewar ginin ba.

Birnin Tarayya dai na fuskantar ruwan sama kusan kowacce rana, wanda ko a yayin da jami’an agajin ke yunkurin ceto mutanen, ruwan sama ake ta tafkawa.




[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...