Ba rashin adalci ne ‘ya fitar da Shekarau daga PDP ba’

[ad_1]

@Twitter/PDP

Hakkin mallakar hoto
@Twitter/PDP

Jam’iyyar PDP mai hamayya a Najeriya ta musanta zargin da tsohon gwamnan jihar Kano Ibrahim Shhekarau ya yi mata cewa rashin adalcin ta ne ya sa shi ficewa daga cikn ta.

Malam Shekarau ya bar PDP ne ranar Talata da safe bayan ya zargi jam’iyyar da rusa shugabancin ta na jiharsa sannan ta bai wa Sanata Rabi’u Kwankwaso -wanda bai dace da komawa cikin ta ba – mukamai mafi tsoka a cikin kwamitin wucin gadin da ta nada a jihar.

Sai dai Malam Shehu Yusuf Kura, kakakin shugaban PDP na Najeriya, ya shaida wa BBC cewa tsohon gwamnan na Kano yana tattaunawa da gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje da zummar komawa APC.

“Tun sati takwas zuwa tara da suka gabata mun san yana magana da APC, mun san yana tattaunawa da gwamnan jihar Kano a kan mukamai da za a ba shi,” in ji Shehu Yusuf Kura.

Sai dai BBC ba ta tabbatar da wanan zargi nasa ba, kuma ya zuwa yanzu Malam Shekarau bai bayyana jam’iyyar da zai koma ba.

Kakakin shugaban na PDP ya kara da cewa a shekarar 2014 lokacin da tsohon gwamnan na jihar Kano ya koma PDP daga APC an yi masa goma ta arziki inda aka mika masa jagorancin jam’iyyar duk da yake ya taras da wasu manyan ‘yan siyasa a cikin ta.

A cewar a, bai kamata Malam Ibrahim Shekarau ya yi korafi ba don an ce za a bai wa bangaren Sanata Kwankwaso wasu mukamai a PDP “tun da ya shigo jam’iyyar tare da ‘yan majalisa da tsohon mataimakin gwamna da sauran manyan ‘yan siaysa.”

Da ma dai masana harkokin siyasa na ganin Malam Shekaau da Sanata Kwankwaso ba za su taba zama a inuwa daya ba saboda tsananin sabanin siyasar da ke tsakani su.

[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...