Ba a biya kudi ba kafin sako ‘yan matan Dapchi – Gwamnatin Najeriya

[ad_1]

A watan Fabrairu aka sace daliban daga makarantarsu da ke Dapchi, a jihar Yobe

Hakkin mallakar hoto
Reuters

Image caption

A watan Fabrairu aka sace daliban daga makarantarsu da ke Dapchi, a jihar Yobe

Gwamnatin Najeriya ta musanta rahotannin da ke cewa ta biya mayakan Boko Haram ‘makudan kudin fansa’ kafin su sako ‘yan matan Dapchi.

Wani rahoto ne da aka gabatar a gaban kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa sai da gwamnatin kasar ta biya “makudan kudi” don kubutar da ‘yan matan makarantar sakandaren garin Dapchi.

Har ila yau rahoton ya ce irin wadannnan kudaden da ake biya suna kara taimakawa wajen wanzuwar ayyukan ta’addanci a yankin Tafkin Chadi.

Fiye da ‘yan mata 100 ne wani bangare na kungiyar Boko Haram ya sace a wata makarantar sakandaren garin Dapchi a jihar Yobe a watan Fabrairun da ya gabata.

Sai dai kimanin ‘yan mata 105 kungiyar ta saki daga bisani, amma kawo yanzu akwai guda da ta rage a hannun mayakan kungiyar wato Leah Sharibu.

Bayan soko ‘yan matan dai Ministan Yada Labaran kasar Lai Mohammed ya shaida wa manema labarai cewa, ba a biya ko da sisin kwabo ba, gabanin sako ‘yan matan a watan Maris din da ya gabata.

Hakazalika bayan fitar rahotan Majalisar Dinkin Duniyar, a ranar Alhamis ministan ya kara jaddada matsayinsa na farko.

“Bai kamata wani ya ce Najeriya ta biya kudi kafin ceto ‘yan matan Dapchi, ba tare da nuna kwararan hujjoji da za su tabbatar da hakan ba,” kamar yadda wata sanarwa da mai taimaka masa Segun Adeyemi ya fitar ta ce.

Lai ya kalubanci duk wani da ke hujjoji da ke nuna cewa an biya kudin da ya bayyana wa duniya hakan.

Har ila yau ya ce “to idan kuma babu hujjojin da za su gasgata hakan to abin ya zama shashi-fadi ke nan.”

Hakkin mallakar hoto
Amsami Ali

Image caption

An kai matan Abuja a cikin motoci

  • A ranar 19 ga Fabrairu aka sace ‘yan matan
  • Dalibai 110 aka sace a makarantar Dapchi
  • An sace su kwana daya bayan sojoji sun fice
  • An shiga rudani kan sace ‘yan matan
  • Da farko an ce ‘yan matan sun shiga daji ne domin buya
  • Sai da aka dauki tsawon mako daya kafin gwamnati ta amince an sace su
  • Gwamnatin Yobe ta yi ikirarin ceto ‘yan matan, kafin daga baya ta nemi afuwa
  • Bangaren Abu Musab al-Barnawi ne ake tunanin sun sace ‘yan matan
  • Boko Haram ba ta fito ta yi ikirarin sace ‘yan matan ba
  • Sace ‘yan Matan Dapchi ya tuna wa duniya da ‘yan matan Chibok
  • Wannan ya nuna har yanzu Boko Haram barazana ce
  • Sun gana da Shugaba Buhari

Jam’iyyar PDP mai hamayya a kasar ta yi zargin cewa jam’iyyar APC da fadar shugaban kasa ne suka kitsa sace matan domin cimma burin siyasa.

Sai dai APC ta musanta zargin, tana mai cewa idanun PDP sun rufe ta kasa fahimtar irin nasarar da take samu a yaki da Boko Haram.

Hakkin mallakar hoto
Amsami Ali

Image caption

Sun kwashe sama da wata daya a hannun mayakan Boko Haram

[ad_2]

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...