Atiku ya isa Najeriya bayan ya bar Amurka

Atiku Abubakar

Hakkin mallakar hoto
@GcfrNg

Atiku Abubakar, tsohon shugaban Najeriya kuma dan takarar shugaban kasa a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, ya sauka a Abuja bayan ziyarar kwana biyu da ya kaiAmurka.

Rahotanni daga Najeriya sun ce ya dawo ne domin muhawarar da aka shirya gudanarwa tsakanin ‘yan takarar shugaban kasa a Abuja a ranar Asabar.

Sai dai babu wani tabbaci daga dan takarar na PDP ko kuma daga jam’iyyarsa kan ko zai halarci muhawarar da za a yi misalin karfe 7 na dare.

Ziyarar dai ta janyo ce-ce-ku-ce tsakanin ‘yan Najeriya musamman kan batun cewa ba zai iya shiga Amurka ba.

Wasu na ganin wannan dalilin ne ya sa Atiku zuwa Amurka domin toshe bakin ‘yan adawa.

Dan takarar na PDP ya wallafa a Twitter cewa ya samu ganawa da ‘ya’yan jam’iyyar PDP a Washington domin neman goyon bayansu ga manufarsa ta gyara Najeriya.

Ya kuma ce ya gana da ‘yan kasuwa domin tattauna hanyoyin ciyar da Najeriya gaba.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...