Asusun Horar Da Ma’aikata Na ITF Ya Hada Gwiwa Da Majalisar Dinkin Duniya

[ad_1]

Da yake jawabi a wani taron manema labarai a Abuja, darakta janar na

hukumar Joseph Ari ya ce akwai guraben aiki da dama a Najeriya

musamman a bangarorin sana”o”in hannu, to amma Najeriyar bata da

kwararrun da zasu cike guraben. Hakan ya sa asusun na ITF ya shiga wani hadin gwiwa da majalisar dinkin duniya don tabbatar da an horas da isassun matasan da zasu cike wadannan gurabe da ake dasu a kasar.

Joseph Ari yace tuni asusun itf baya ga dubban dubatan matasan da tuni suka horas yanzu haka an tsara sake horas da Karin wasu dubu goma sha uku, kana ya nemi suma gwamnatocin jihohi da su dau nauyin horas da Karin matasan don samar da ayyukan yi.

Darakta janar na ITF din yace ta hanyar sana”o”in hannu ne kadai za a

tabbatar an samar da isassun aikin yi ga matasan Najeriya, domin a

cewar sa gwamnati ita kadai ba zata iya samar da aiki ga kowa da kowa

ba. Daga nan ya nuna rashin jin dadi ganin yadda yan kasashen waje ke

mamaye wuraren aikin da ya kamata ace yan Najeriya ne ke yinsu.

Yayin da yake tsokaci dangane da yadda wasu ke ganin hukumarsa na aiki

iri guda da na hukumar samar da aikinyi ta kasa wato NDE da sauran

hukumomi makamantansu, Sir Joseph Ari yace zai kyautu

azo a zauna a dandale don tantance irin ayyukan da kowacce hukuma

zatafi mayar da hankali akai.

[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...