APC ta sake dage ranar gudanar da zaben fidda gwanin dan takarar shugaban kasa

Jam’iyar APC ta sake dage ranar da zata gudanar da zaben fidda gwani na shugaban kasa daga ranar 25 ga watan Satumba ya zuwa ranar 27 ga Satumba.

Yekini Nabena mai rikon muƙamin kakakin jam’iyar shine ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

Nabena ya kuma ce yan jam’iyar su tabbatar sun karbi katun shedar jam’iyarsu na din-din daga mazabunsu.

“Zaben fidda gwanin shugaban kasa na kai tsaye da aka shirya gudanarwa ranar Talata 25 ga watan Satumba,2018 yanzu zai gudana ranar Alhamis 27 ga watan Satumba, 2018,” sanarwar ta ce.

“Cikakkun yan jam’iyar masu rijista za su karbi katin kasancewarsu mamba na dindindin daga mazabunsu.”

Babu wani dalili da aka bayar na wannan canji da aka samu.

Shugaban kasa Muhammad Buhari shine ɗan takara daya tilo da ya tsaya a zaɓen.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...