Gwamnan ya bayyana hakan ne ta shafinsa na Twitter, sai dai ba duka sassan jihar ba ne aka sassauta dokar.
An sassauta dokar a birnin Kaduna, inda a yanzu dokar za ta fara aiki daga karfe 5 na yamma zuwa karfe 1 na rana.
Wannnan na nufin kenan mutane za su iya zirga-zirgansu da harkokinsu a birnin tsakanin karfe 1 na rana zuwa karfe 5 na yamma.
Har ila yau, gwamnan ya ce akwai unguwannin da dokar hana fita za ta cigaba da aiki wadanda su ne Kabala West da Kabala Doki da Narayi da Maraban Rido.