An sassauta dokar hana zirga-zirga a Kaduna

Gwamnna Kaduna Nasir El-Rufai

A yau Talata, Gwana Nasir El-Rufai ya jagoranci taron majalisar tsaro ta jihar

Gwamna jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya sanar da sassauta dokar hana fita ta sa’a 24 da aka sanya a jihar ranar Lahadi.

Gwamnan ya bayyana hakan ne ta shafinsa na Twitter, sai dai ba duka sassan jihar ba ne aka sassauta dokar.

An sassauta dokar a birnin Kaduna, inda a yanzu dokar za ta fara aiki daga karfe 5 na yamma zuwa karfe 1 na rana.

Wannnan na nufin kenan mutane za su iya zirga-zirgansu da harkokinsu a birnin tsakanin karfe 1 na rana zuwa karfe 5 na yamma.

Har ila yau, gwamnan ya ce akwai unguwannin da dokar hana fita za ta cigaba da aiki wadanda su ne Kabala West da Kabala Doki da Narayi da Maraban Rido.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...