An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta jihar Filato.

Mai magana da yawun rundunar samar da tsaro a jihar Plateau ta Operation Safe Haven, Kaftin Oya James shi ne ya sanar da haka ga manema labarai.

Marigayin shi ne ke riƙe da sarautar Ciroman Kumbun dake gudumar Magun.

Shugaban kungiyar Gan Allah Fulani Development Association of Nigeria, (GAFDAN) Garba Abdullahi ya fadawa jaridar Daily Trust cewa marigayin ya ɓace bayan da ya bar asibiti domin ya sayowa matarsa da aka kwantar abinci.

“Bayan bincike na kwana huɗu an gano gawar a wata rijiya da ba a amfani da ita dake kusa da asibitin” a cewar Garba.

Shugaban ya shawarci mutanensu da su kwantar da hankali kuma kada su ɗauki doka a hannunsu.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...