An kori ɗan sanda a Najeriya saboda karɓar kuɗi a hannun mutane ba bisa ka’ida ba

Rundunar ‘yan sandan jihar Ribas ta ce ta kori ɗaya daga cikin jami’anta mai suna Insifekta Michael Odey da ke da hannu wajen karbar kudi a hannun wani.

Hakazalika, ta bayyana cewa an gurfanar da wasu jami’an biyu da ke da hannu a wannan aika-aika tare da ba da shawarar a kore su kamar yadda aka tsara.

A Najeriya an dai saba ganin irin wannan tsakanin jami’an ƴan sanda, wato karɓar kuɗi a hannun mutane.

Wannan irin halayyar ta karɓar ba bisa ka’ida ba na daya daga cikin abubuwan da haddasa zanga-zangar #EndSARS wacce ta jawo hasara sosai.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...