An gudanar da zanga-zangar goyon bayan Abba Gida-gida a Ibadan

A jiya Lahadi ne wasu magoya bayan gwamnan jihar Kano, Abba Yusuf, suka yi dandazo a harabar wasanni ta Lekan Salami dake birnin Ibadan a jihar Oyo domin gudanar da addu’o’i tare da gudanar da zanga-zangar lumana domin mika musu bukatunsu na ganin Abba Kabir ya cigaba da zama gwamnan jihar Kano.

Rahotanni sun nuna cewa kotun daukaka kara ta tabbatar da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Kano ta yanke, wadda ta soke nasarar Yusuf tare da bayyana dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress, Nasiru Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben.

A makon da ya gabata ne zanga-zangar ta barke a Kano sakamakon samun sabani a cikin kwafin ainihi na hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke na korar Yusuf.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...