[ad_1]
Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta sanar da cewa Amurkar za ta daina bayar da duk wani tallafin kudi ga Hukumar bayar da agaji ta Majalisar Dinkin Duniya mai tallafawa ‘yan gudun hijirar Falasdinu.
Ta kuma ce hukumar ta UNRWA na da rauni wanda ba zai iya gyaruwa ba.
Wani mai magana da yawun Hukumar ta UNRWA, Chris Gunness ya kare hukumar a jerin sakonni da ya wallafa a twitter. Ya ce “Ba za mu amince da sukar da a ke yi wa hukumar na cewa makarantunta da cibiyoyin lafiyarta da tsare-tsarenta na agajin gaggawa na da raunin da ba za a iya gyarawa ba.”
Wani mai magana da yawun Shugaba Mahmoud Abbas ya ce matakin da Amurkar ta dauka wani salo ne na horo, kuma zalunci ne ga al’ummarsa.
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya ya yi kira ga sauran kasashen duniya da su cike gibin dala miliyan dari uku da hukumar bayar da agajin ta ke da shi.
Dangantaka tsakanin Amurka da Shugabannin Falasdinu ta tabarbare a ‘yan watannin nan, musamman ma tun da Shugaba Donald Trump ya yanke shawarar mayar da ofishin jakadancin Amurka birnin Kudus.
A watan Janairu ne dai Shugaban Amurkar Donald Trump ya bayyana cewa zai kawo wasu sauye-sauye saboda yankin na Falasdinu ba ya mutunta Amurka duk da makudan kudin da ta ke samarwa domin aikin agaji a yankin.
[ad_2]