Akwai ‘maciya’amana’ cikin ma’aikatan EFCC —Magu

[ad_1]

Ibrahim Magu

Hakkin mallakar hoto
Facebook/EFCC

Image caption

Ibrahim Magu ya ce za a hukunta maciya amana a cikin jami’an hukumar idan aka kama su

Shugaban hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya zagon kasa, Ibrahim Magu, ya ce akwai wadanda ake zargin maciya amana ne cikin ma’aikatan hukumar wadanda ke fallasa ayyukan hukumar ga ‘yan siyasa.

Magu, wanda ya fadi hakan a wajen wani taro na masu ruwa da tsaki a harkar yaki da cin hanci da rashawa, ya ce, hukumar tana bincike game da ire-iren wadannan jami’an.

Ya kara da cewa da zarar an gano irin wadannan jami’an a hukumar, za a hukunta su.

Magu ya ce irin nasarorin da hukumar ta samu a kotu kan tsofaffin gwamnoni biyu ya nuna cewa hukumar tana taka rawar gani wajen yaki da cin hanci da rashawa.

Shugaban hukumar ya ce irin wadannan nasarorin za su zama izina ga duk mai son halatta kudin haram a kasar.

Sai dai kuma tun ba yau ba wasu daga cikin ‘yan siyasa dake jam’iyyar hamayya ke ikirarin cewar EFCC tana nuna son kai wajen yakin da take yi da cin hanci da rashawa.

Kuma suna ikirarin cewar ba ta kama ‘yan jam’iyyar APC mai mulki.

Da aka yi masa tambaya game da wannan, sai shugaban hukumar ya ce babu ruwan EFCC da siyasa, kuma zargin ba zai hana hukumar yaki da cin hanci da rashawa ba.

[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...