[ad_1]
Wata gagarumar girgizar kasa mai girman digo shida a ma’aunin karfinta ta afkawa yammacin kasar Iran dake da iyaka da makwafciyar ta ta kasar Iraq da safiyar ranar Lahadi.
Kamar yadda muka samu labari girgizar kasar wadda ta mamaye kusan kilomita 26 a garin Javanrud dake a jihar Kermanshahta mutane sama da 200 ne suka jikkata.
Kasar Iran dai dake a yankin gabas ta tsakiya na zaman babbar hedikwatar musulmai mabiya darikar Shi’a kuma suna da’awar tabbatar da shari’ar muslunci ne kamar kasar Saudiyya.
[ad_2]