[ad_1]
Jam’iyyar PDP ta sanar da komawar gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Waziri Tambuwal Tare da Mataimakin Gwamnan jihar kano, Farfesa Hafizu Abubakar yau.
Jam’iyyar PDP ta bayyana hakan a shafin ta na tuwitta a yammacin yau inda ta bayyana komawar Tambuwal da Farfesa Hafizu Abubakar.
A baya bayan nan ne dai wasu ƙusoshin jam’iyyar APC suke ta canza sheƙa zuwa jam’iyyar PDP wanda suka hada Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki tare da Tsohon Gwamnan Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso.
[ad_2]