Kotu ta soke dukkanin zaɓukan fidda gwani na jam’iyar APC a jihar Rivers

Wata babbar kotu dake birnin Fatakwal da mai shari’a Chiwendu Nwogu ke jagoranta a ranar Laraba ta rushe shugabancin jam’iyyar APC na jihar da Ojukaye Amachree ke jagoranta.

Kotun ta kuma soke zaben fidda gwanin takarar gwamnan jihar da Tonye Cole ya lashe inda ta ce zaben da aka yi masa ya sabawa kundin tsarin mulki.

Haka kuma kotun ta soke zabukan fidda gwani na yan majalisar wakilai ta tarayya, yan majalisar dattawa da kuma na yan majalisar dokokin jihohi da jam’iyar ta gudanar a jihar Lagos.

Har ila yau kotun ta kuma soke zaben shugabannin jam’iyar na mazabu da kuma na kananan hukumomi da shugabancin jam’iyyar ya gudanar.

Wasu mutane ne suka shigar da kara gaban kotun suna kalubalantar yadda aka gudanar da zabukan shugabannin jam’iyar inda suka ce zabukan sun saba sharuda da kuma kundin tsarin mulkin jam’iyar PDP.

More News

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...