Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar Delta.

Rahotanni sun tattaro cewa barayin sun gaza a yunkurin sace matar ne a ranar 2 ga Satumba, 2024, a mahadar Okoloba, titin Jakpa, Uvwie, inda masu garkuwa da mutanen suka kashe ‘yan sanda biyu da direban, Mista David Imela, a yayin da lamarin ya faru.  .

Sai dai mai magana da yawun ‘yan sandan, Bright Edafe, ya tabbatar da faruwar lamarin wa manema labarai a ranar Lahadi a Asaba, babban birnin jihar Delta.

Ya ce, “Bayan yunkurin yin garkuwa da matar daya daga cikin ‘yan majalisar dokokin jihar Delta da bai yi nasara ba, inda wadanda ake zargin masu garkuwa da mutane ne suka kashe ‘yan sandan mobal biyu da direban, kwamishinan ‘yan sanda, Olufemi Abaniwonda, nan take ya bayar da umarnin tura jami’an tsaro ba tare da ɓata lokaci ba.”

Ƴansanda sun kuma ƙwace wasu makamai daga hannun ƴanbindigar.

More News

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...

Gwamnati za ta fara biyan ma’aikata naira 30,000 mafi ƙarancin albashi a Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya sanar da cewa za su fara aiwatar da tsarin mafi ƙarancin albashi naira 30,000 ga ma'aikatan jihar...