Ƙungiyoyin ƙwadago sun dakatar da yajin aikin na wani dan lokaci bayan Ribadu ya shiga tsakani

Kungiyoyin kwadagon Najeriya NLC da TUC sun dakatar da yajin aikin da suke yi a fadin kasar na wani dan lokaci sakamakon shiga tsakani da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu ya yi.


Matakin da aka bayyana bayan taron na sa’o’i daya, ya nuna yadda kungiyoyin suka amince da kudurin Ribadu na magance matsalolinsu ba tare da nuna son kai a siyasance ba.

Mataimakin shugaban TUC na kasa, Tommy Etim, ya bayyana cewa dakatarwar na wucin gadi ne, har zuwa lokacin da gwamnati za ta amsa bukatunsu.

Yajin aikin dai ya samo asali ne sakamakon cin zarafi da aka yi wa shugaban kungiyar NLC, Joe Ajaero, a lokacin wata zanga-zanga a jihar Imo.

Al’ummar kasar na jiran karin bayani yayin da dakatarwar ta wucin gadi ta ta’allaka ne kan ayyukan gwamnati cikin wa’adin da aka kayyade.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...