Ƴan fashin daji sun kashe ɗan sanda ɗaya a wani shingen bincike a Zamfara

Ƴan fashin dajin a ranar Lahadi sun kai da farmaki kan wani shingen binciken ƴan sanda inda suka kashe ɗan sanda guda ɗaya tare da jikkata Wasu.

Shingen binciken an kafa shi ne tazarar  ƙasa da kilomita ɗaya kafin ka isa Kwatarkwashi garin dake kusa da Gusau babban birnin jihar.

Majiyoyi da dama sun faɗawa jaridar Daily Trust cewa ƴan fashin dake kan babura sama da 40 sun kai farmakin ne da misalin ƙarfe 04:00 na asubahin ranar Lahadi.

Ƴan fashin sun ƙona duk wani mai muhimmanci da suka samu a shingen binciken kafin su  bar wurin.

A cewar wata majiya ƴan fashin dajin sun samu nasarar fin ƙarfin ƴan sandan abun da yasa wasu daga cikinsu suka tsere bayan an ɗauki lokaci suna musayar wuta.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...