Ziyarar Atiku: Garin kano ya yi cikar kwari

Garin Kano ya yi cikar kwari yayin da dantakarar shugaban kasa Atiku Abubakar ke ziyarar yakin neman zabe.

Tituna da dama dake birnin sun shafe makil da mutane dake sanye da jar hula dake nuna biyayya ga darikar Kwankwasiya.

Dantakarar shugaban kasar da tawagarsa sun shafe sa’o’i da dama akan hanya kafin su isa fadar Sarkin Kano Muhammad Sunusi.

Daga filin jirgin saman Malam Aminu Kano ya zuwa fadar sarkin tafiya ce da ba tafi mintuna 30 amma sai da tawagar ta shafe sama da sa’o’i 3 saboda da cinkoson jama’a.

Shin ko hakan na nufin karɓuwa da Atiku ya yi a Kano zabe ne kawai zai bayyana haka.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Rundunar dakarun soja ta ƙasa da ƙasa wato Multi National Task Force(MNJTF) a turance shiya ta 3 dake Monguno a Najeriya ta bayar da...

Sojoji a birnin Ibadan  sun kama Æ´an fafutukar kafa Æ™asar Oduduwa

Dakarun rundunar sojan Najeriya  sun samu nasarar kama wasu mutane masu fafutukar kafa ƙasar Oduduwa a birnin Ibadan na jihar Oyo. Masu fafutukar sanye da...