Zaman fursuna na shekara 3 ko tarar $3,000 ga masu shan shisha

shisha

Wuraren da ake shan tabar shisha a Ghana za su dinga fuskantar hukunci mai tsanani idan har ba su bi dokokin kiyaye lafiya da kasar ta tanadar ba.

Shan tabar Shisha dai ya zama ruwan dare a tsakanin matasa a kasar.

Sai dai akwai sabanin ra’ayi kan cewa tabar shisha ba ta da illa kamar taba sigari.

Amma Hukumar Lafiya Ta Duniya WHO da Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Ghana FDA, ba su yarda da wannan batu ba.

Hukumar ta ce daga yanzu duk mai mashayar da aka kama ana shan shisha a wajen zai fuskanci zaman gidan yari na shekara uku ko a ci shi tarar dala dubu uku, kwatankwacin naira miliyan daya da 80,000 kenan.

Sai dai wannan hukunci zai hau kansu ne kawai idan ba su yi rijistar shishar ba ko kuma idan ba su sanya sanarwar gargadi kan irin hadarin da ke tattare da shanta yake ba.

Yayin shan shisha

Shan wannan taba mai kanshin gaske na kara karbuwa a wurin jama’a a fadin duniya, amma masana harkar lafiya sun ce mafi yawan wadanda suke shanta ba su san hadarin da ke tattare da hakan ba.

Yanzu dai mutane ne da dama suke cin moriyar wannan taba wadda ke tashe a Indiya da Gabas ta tsakiya inda aka ce daga nan ta samo asali.

A Gabas ta tsakiya yayin ya ratsa har tsakanin ‘yan yara maza da mata da ma manyan mata wadanda yawancinsu ba sa shan taba.

Wannan yayi yanzu ya kai har ga kasashen Turai da Brazil da kuma Amurka inda za ka ga shagunan shan wannan taba mai zamani.

Shugaban sashen tiyatar zuciya a babban asibitin kasa na Saudi Arabia, National Guard Health Affairs, Farfesa Hani Najm, ya taba sheda wa BBC a wata tattaunawa cewa yana fargaba shan tabar shisha zai iya kara yawan masu cutukan zuciya a kasashen yankin Gabas ta tsakiya.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...